SALLOLI BIYAR NA YINI SUNA KARA LAFIYA MAI INGANCI GA JIKIN DAN ADAM.

SALLOLI BIYAR NA YINI SUNA KARA LAFIYA MAI INGANCI GA JIKIN DAN ADAM. 


Hakika Salloli biyar da mukeyi ayini a kowace suna  karawa dan Adam lafiya  da kuma kara  bude  masa  kofofin samu, bayan  ladar  da zai samu.
Sannan  kuma  Suna  karawa mutum  kusanci  gun  Allah da tsoronsa
1- sallar Asubah: tana karawa mutum kyan hali da kyan fuska
2- sallar Zuhur: tana kara budewa mutum kofofin samu.

3- sallar Asari: tana kara lafiya  ingantacciya a jikin mutum. 

4- sallar Magrib: tana rigewa mutum fargaba da damuwa a zuciya.

5- sallar Isha’i: tana sa mutum bacci  maidadi  cikin amincin Allah.

Allah kabamu ikon juriya  da jajircewa wajen yawaita ibadun Allah don neman  tsira da lafiya  ingantacciya.

KASHE-KASHEN AURE

                                                   KASHE-KASHEN AURE










Aure ya kasu kashi-kashi. Akwai auren soyayya; da auren tilas, da auren zumunta, da auren sadaka,  da auren ɗiban wuta, da auren dangana-sanda, da, auren gayya, da auren ɗiban haushi ko ɗiban takaici, da ɗiban tsiwa ko kece raini, da kashin ƙwarnafi, da sauran irinsu.
Auren Soyayya: Aure ne wanda yaro ke ganin yarinya ya ce yana sonta da aure, ita kuma ta amince, iyayenta ma su yarda da maganar, kana a yi haramar ɗaurin aure.
Auren Tilas: A nan, yaro yakan ga yarinya ne, ya ce yana son ta da aure, amma ba ta amince ba. Iyayenta kuma su zartar da hukunci, walau wasu na so, ko suna ƙi. Har ma akan ba da yarinya ga wanda yake sa’an mahaifinta ne, ko sa’an kakanta, alhali kuma ba ta so. Kuma akan nema wa yaro yarinya ba tare da yana so ba, saboda wata alaƙa ko yarjejeniya tsakanin iyayensu. Wannan ma auren tilas ne.
Auren Zumunta: Wannan aure ne wanda akan nema wa yaro yarinya daga cikin dangin uwa ko na uba, ba tare da an shawarci yarorn ko yarinyar ba. Irin wannan aure, ana yin sa ne don ƙara yauƙaƙa danƙon zumunta tsakanin ‘yan’uwa.
Auren Sadaka: Shi kuma aure ne da ake bayar da yarinya ga wani, saboda neman tubarraki, kamar irin sadakar da ake ba malamai, almajiransu, musamman idan yarinya ta girma bata sami manemi da wuri ba. Ana kuma yin auren sadaka don gudun kada ta jawo wa iyayenta abin kunya. Wani lokaci kuma idan mutum bai sami haihuwa da wuri ba, yakan yi alƙawarin cewa, zai ba da ita sadaka in ya samu. Yakan ba wani, ya ce, in ya sami ‘ya har ta rayu, zai yi sadaka da ita.
Auren Ɗiban Wuta: Bayan an saki mace saki uku, alhali kuwa matar tana son mijinta, shi ma yana son ta, dole sai ta auri wani mutum, kafin ta sami damar komawa ga mijinta na farko. To, auren nan da ta yi, da ƙudurin cewa za ta dawo wurin mijinta na da, wannan shi ne auren ɗiban wuta.
Auren Dangana-Sanda: Mutum yakan auri matar da ke zaune a gidan kanta; Sai ya zamana ba za ta iya tasowa ta zo gidansa ta zauna ba, saboda waɗansu dalilai. Haka shi ma ba zai iya zuwa gidanta ya zauna ba. Sai dai ya riƙa zuwa can gidanta yana kwana. Irin wannan aure, abinda ya sa ake kiran sa auren dangana-sanda, wai saboda maigida yana dangana sandarsa a bakin kofar dakinta ne, kana ya shiga ya kwana.
Auren Gayya: Idan matar mutum ta fita, alhali kuwa yana son ta, ya dai sake ta ne don ta addabe shi, to maza sai ya yi sauri ya yi wani aure kafin ya sake ta, ko kafin ta gama idda. Ba don komai zai yi wannan auren ba, sai don kurum ya fashe haushinsa, ko kuma don kada matar ta riga shi yin aure.
Auren Ɗiban Haushi: Ana kuma kiran sa auren ɗiban takaici, ko auren ɗiban tsiwa, ko na kece raini da kashin ƙwarnafi. Idan matar mutum ta dame shi da fitina, yakan tashi takanas ya je ya auri wata mace mai kyau ko dukiya ko asali ko addini, fiye da wadda ke gidansa, ko wadda ya saki. Ana yin wannan aure don kawai fashe haushi ko ɗebe takaici ko don a gusar da walakanci da raini da tsiwace ­tsiwace na ba gaira ba dalili.

AURE








AURE

Aure alaƙa ce ta haliccin zaman tare tsakanin namiji da mace. Ana yin sa ne saboda abin da aka haifa ya sami asali, da mutunci, da kiwon iyaye. Kuma shine maganin zina da ‘ya’ya marasa iyaye. Aure muhimmin abu ne ga al’umma. Saboda haka akwai hanyoyi ayyanannu na tabbatar da shi.
Idan yaro ko yarinya suka girma sai iyayensu su sa ransu su yi musu aure tun ransu bai yi halinsa ba.
Wani lokaci kuwa yaro ne yake ganin yarinya ya riƙa yi mata ‘yar kyauta har a gane yana son ta, sai a nemar masa ita, ko abokansa su faɗa wa iyayensa a gida cewa sun ga alamar Wane yana son Wance. Ko kuma a faɗa wa yarsa ko gwaggonsa, ko matan wansa, su kuma su isar da saƙon ga iyayensa.


   Aure,
    abune wanda ake yi tsakanin mace da namiji domin gudanarda wata sabuwar rayuwa tsakanin na miji da amce.
  Aure,
  abune wanda ake yinsa badan rabuwa da juna ba ko zama na dan wani lokaci shi aure anayinsane da niyar zama har abada tareda juna. 

SALLAR IDI

SALLAR IDI

Sallar idi ita ce taron da ake yi sau biyu ko sau uku a shekara, watau a ƙaramar Sallah, saboda murnar ƙarewar azumin watan Ramalan lafiya, da kuma Babbbar Sallah, saboda murnar ƙarewar aikin hajji lafiya. A wasu wuraren kuma ana yin Sallar Gani, ko Sallar Mauludi, don tunawa da ranar da aka haifi Manzon Allah, Annabi Muhammadu ( tsira da Amincin Allah Su tabbata a gare shi). Sai dai ita wannan sallar ba a yi mata idi, watau ba a zuwa bayan gari a yi raka’o’in sallah.
Tun kafin jajibirin sallolin nan ake ta yin kintse-kintse, ana tattalin harkokin sallah, ana dake-dake, da sayen bisashe, da sauran kayan jin daɗi. A daren jajibiri ake ta yi wa sarakunan gargajiya bushe-bushe da kaɗe-kaɗe, ko buga tambari, ko a daka (bindiga) saboda a sanar da cewa go be sallah. Kowane babban mutum yakan sanar ta hanyar gangami, ko aikawa da kar-ta-kwana, da sauran hanyoyin sadarwa irin na gargajiya.
A safiyar sallah akan yi ta raba tuwaye kuma ‘yan’ uwa da maƙwabta sukan tara abinci iri-iri a gidan ɗayansu, a taru a ci tare wuri ɗaya, ana ci ana raha. Idan ƙaramar Sallah ce, akan ci abincin tun kafin a tafi Masallacin Idi. Amma idan Babbar Salla ce, sai an sauko Idi. Wajen abinci kuwa, kowane mai gida yakan yi iyakar ƙoƙarinsa gwargwadon ikonsa, ya ga dai ya fifita abincin sallah, ya daɗaɗa shi fiye da wanda ya saba ci yau da kullum.
Ahantsin ranar idi, mutane sukan fita; har da yara da tsofaffi, su tasar wa filin idi a bayan gari, inda za a jira sarki, da limamin gari don sallah. Ana cikin jira ne sarki da baradensa, da hakimansa, na kusa da na nesa sukan iso a kan dawakai da taguwoyi, kowannensu ya ci ado, suna tafiya suna takama saboda murnar zuwa Masallacin Idi da kewayowar wannan rana.
Da zarar sarki ya isa masallaci sai a tsayar da sallah, a yi raka’o’i biyu a sallame. Wasu mutane su yi tafiyarsu, wasu kuma su dakata don su saurari huɗubar liman, wadda galibi yake gargadin jama’a, da jawo hankalinsu zuwa ga kulawa da addini, da tuba ga Allah, tuba ta sosai, da gyara halaye, da lura da wa’aztuwa da juye-juyen zamani da sauran irinsu.
Bayan ya ƙare huɗuba, sai kowa da kowa ya kama gabansa, ya tafi gida ya ci gaba da hidimar sallah. Sarki da manyan mutane sukan bi wata hanya ba wadda suka biyo da farko ba, saboda kowa da kowa ya sami damar ganin su, don su yi murna da ganin sarki da kewayowar wannan rana mai albarka. A daidai wannan lokaci kuma, wasu jama’a maza da mata, yara da manya, suna can suna taruwa kan wuri a fadar sarki, suna jiran sa. Idan sarki ya isa fada tare da jama’arsa, sai ya hau sama idan a birni ne, don mutane su gan shi, shi kuma ya gan su ya yi musu jawabin cikar shekara, inda yake jan kunnuwansu da hada kai da son zumunta da zama lafiya, da kula da aiki da addini, da al’ada, da ladabi da biyayya ga magabata, da cika alƙawari, da tsare mutunci, da kula da tsabtar jiki data gidaje da sauransu, Bayan sarki ya yi jawabi, sai ya shiga gida ya zauna a kan karagar mulki, hakimai da duk mutane suna tafiya dai-dai suna gaisuwa yana karɓa. Idan ƙauye ne sai kawai ya shiga soro ba da ya hau ko’ina ba, ana zuwa wurinsa yana karɓar gaisuwa.
Wannan taro, na farkon rana, ya fi cika a ƙaramar Sallah,saboda rashin hidimar yanke-yanken dabbobin layya.
Da an ce marece ya yi, sai dandalin gidan sarki ya cika da mutane faƙil, ko’ina, ba masaka tsintsiya, ana ta kade-kade da bushe-bushe. Samari da ‘yammata ana kalankuwa, ana darawa, ana tafawa ana murna, da farin ciki. Yara kuma su yi ta zaci sunakai da komowa harwajen kwanabiyar ko bakwai.
Yawon Sallah: Mutane suna zuwa suna gai da ‘yan’uwa da abokai da surukai, don taya su murnar kewayowar ranar sallah. Su kuma sukan ba su goron sallah. Yara da yawa sukan mayar da yawonsalla tamkar wani abin ku zo ku gani suna shiga gida-gida, suna kaɓiar abin yawon sallah, kuma suna tafiya suna yi wa juna ba’ar raha iri -iri.
Rana ta biyu, a kashegarin sallah, sai sarki yakan yi hawa, wanda ake kira hawan sarki, ya kuma ci gaba da hawan har kwana uku don ya sadu da mutanensa, ya ga wasu wurare. Wannnan hawa, a wasu wurare sunansa hawan daushe , ko hawan bariki.
Shi ke nan, sai a ci gaba da shagulgulan sallah har ‘yan kwanaki, sa’annan kowa ya koma ga harkar gabansa ta yau da kullum.
“Sallah bukin ɗaya rana! Sallah mai yawan baya, kin wuce kin bar wawa da bashi!”

AL'ADU

AL’ADUN HAUSAWA

Hausawa mutane ne masu tsananin rikon al’adunsu na gargaiiva, musamman wajen tufafi, da abinci, da al’amuran da suka shafi aure ko haifuwa, ko mutuwa, da sha’anin mu’amala tsakanin dangi da abokai da sbuwagabaam da sauransu, da kuma al’amuran sana’a ko kasuwanci ko neman ilimi.
Tun daga zuwan Turawa har yau, Hausawa suna cikin al’ummomin da ba su saki tufafinsu na gargajiya su ari na baki ba. Galibin adon namiji a Hausa ba ya wuce riga gari, da wando musamman tsala, da takalmi faɗe ko ƙafa-ciki, da hula ƙube, ko dankwara, ko dara. In kuma saraki ne ko malami ko dattijo, yakan sa rawani. Adon mata kuwa, zane ne, da gyauton yafawa, watau gyale, da kallabi, da taguwa, da ‘yan kunne, da dutsen wuya, watau tsakiya. A da can, suna sa ɗan hanci, amma yanzu wannan adon ya ƙaura.
Yawancin abincin Bahaushe kuwa, ana yin sa da gero ko dawa ne. Sai kuma sauran abubuwan haɗawa, da na marmari, kamar su wake da shinkafa da alkama, da kayan rafi, da sauransu.
Yawancin Hausawa Musulmi ne, saboda haka yawancin al’adunsu da suka shafi aure da haifuwa da mutuwa, duka sun ta’allaƙa da wannan addini. Sai ɗan abin da ba a rasawa na daga al’adun gargajiya, musamman a wajen Maguzawa.
Haka kuma wajen mu’amala da iyaye ko dangi ko abokai, ko shuwagabanni ko maƙwabta ko wanin waɗannan yawanci na Musulunci ne. Kazalika sha’anunuwan sana’a da kasuwanci da neman ilimi, duk ajikin Musulunci suka rataya,
Can ainihi, sana’a da kasuwanci da neman ilmi suna bin gado ne. Watau kowa yana bin wadda ya gada kaka da kakanni. Kuma idan mai sana’a ya shiga baƙon gari, zai je ya sauka a gidan abokan sana’arsa ne. In ma koyo ya zo yi, zai je gidan masu sana’ar gidansu ne. Saboda haka kusan kowace sana’a akwai sarkinta, da makaɗanta, da mawaƙanta, kai har ma da wasu al’adu na masu yinta da suka sha bamban da na sauran jama’a.
Bauta da barance a wurin Bahaushe ba munanan abubuwa bane, musamman dangane da sha’anin koyon sana’a. Bawa yana fansar kansa ta hanyar sana’a. Kuma mai koyon sana’a yana yin barance a gidan mai koya masa ne. Irin wannan almajircin, ana kiran sa bauta. Duk mai wata sana’a, ko ɗan kasuwa, ko malami, yana alfaharin a ce ga wasu sun koya a wurinsa har sun ƙasaita, ko ma har sun fi shi. Su kuma duk irin maƙamin da suka samu, ba za su raina shi ba. Za su riƙa yi masa ladabi.

How to remove write protection from USB drives and memory cards

Write protection always seems to rear it's ugly head at the worst possible moment but fear not, we've put together a handy guide so you can get around it fast.

by_nazbeen,sok,city

 

 

Write protection being difficult is one of the more frustraiting issues to deal with when you're trying to leave the office for the day. Not being able to move your files over onto a USB stick or drive is the last thing you want to deal with. And you're 100% certain you've got the 'lock' switch in the correct position on the stick, yes?
But just in case this switch is news to you, it is well worth checking that your device has the switch set to 'unlocked'. When set to 'locked' you won't be able to copy any new files on to the memory card or USB stick, and it also stops you from accidentally formatting it. We've all locked our USB without noticing it, don't worry.
You'll still be able to view files which are already stored on the drive, but you can't delete them (they sometimes seem to delete OK, but the next time you check, there they are again!).
But if this isn't the problem, you might still be able to fix things and continue to use your USB flash drive or SD card - we'll explain how.
Unfortunately, in some cases the device may be corrupt or physically broken and no tricks or software will make it work again. The only solution in this case is to buy a new drive. And if you're just trying to get back lost data,


Regedit



In any version of Windows from XP onwards, run Regedit.exe.
If you're not sure how to find it, searching 'regedit' in the Start menu will usually show the program at the top of the list.
It's a bit like File Explorer, so use the pane on the left to navigate to the following key:
Computer\HKEY_LOCAL_MACHINE\SYSTEM\CurrentControlSet\Control\StorageDevicePolicies
Note: if you can't find StorageDevicePolicies, see the next step.
Double-click on the WriteProtect value in the right-hand pane. You can now change the Value data from 1 to 0. Then click OK to save the change. Close Regedit and restart your computer. Connect your USB drive again and, with a bit of luck, you should find it is no longer write protected.
You can now continue to use the drive, but it's worth copying off any files you want to keep and then formatting it by right-clicking on it in the list of drives in File Explorer and choosing Format.

StorageDevicePolicies



If you can’t find StorageDevicePolicies, you can create it by right-clicking in the white space in the 'Control' folder and choosing New -> Key and entering the name StorageDevicePolicies.
Now double-click on the new key (it will show as a folder) and right-click once again in the white space and choose New -> DWORD. Name this WriteProtect and set its value to 0. Click OK, exit Regedit and reboot your computer.
If this method doesn’t work, go to the next step.

Diskpart



With your USB drive or memory card attached to your computer, launch a command prompt. You can do this by searching for cmd.exe or 'Command Prompt' in the Start menu.
Note: you may need to run cmd.exe with administrator privileges if you see an “access is denied” message. To do this, right-click on Command Prompt in the Start menu and choose 'Run as administrator' from the menu that appears.
If you have Windows 10, simply right-click on the Start button (bottom left of the screen) and choose Command Prompt (admin).
Now, at the prompt, type the following and press Enter after each command:
diskpart
list disk
select disk x (where x is the number of your non-working drive – use the capacity to work out which one it is)
attributes disk clear readonly
clean
create partition primary
format fs=fat32  (you can swap fat32 for ntfs if you only need to use the drive with Windows computers)
exit.

 

SALLOLI BIYAR NA YINI SUNA KARA LAFIYA MAI INGANCI GA JIKIN DAN ADAM.

SALLOLI BIYAR NA YINI SUNA KARA LAFIYA MAI INGANCI GA JIKIN DAN ADAM.  Hakika Salloli biyar da mukeyi ayini a kowace suna  karawa dan Ada...